Abd al-Qadir dan Tafa

Abd al-Qadir dan Tafa
Rayuwa
Haihuwa 1804 (220/221 shekaru)
Sana'a
Sana'a marubuci, mai falsafa da maiwaƙe

Abd al-Qadir dan Tafa (1804 – 1863/4), wanda kuma aka fi sani da Dan Tafa, masanin tarihi ne, masanin tauhidi, falsafa, mawaki kuma masanin fikihu daga khalifancin Sokoto. An dauke shi a matsayin "mafi ilimi" a zamaninsa.: 101-102 Ya kasance kwararre mai ilimi wanda ya zurfafa a fannonin ilimi daban-daban,amma ya yi suna musamman wajen rubuce-rubucensa na tarihi da na falsafa.:221  : 221 

Dan Tafa ya rayu ne a lokacin da ake fama da tashin hankali a kasar Hausa,inda ya shaida jihadin Sokoto da kuma kafa Daular Sakkwato daga baya .Bayan rasuwar shugabanni uku masu neman sauyi, Usman,Abdullahi,da Muhammad Bello,Dan Tafa ya zama wanda ake nema ruwa a jallo saboda hikima da kwarewarsa a kan al'amuran tarihi,Musulunci,da jagoranci.Ya taka rawar gani a fannin ilimi ta hanyar gudanar da wata cibiya ta ilimi a Salame wadda ta jawo malamai daga sassa daban-daban na yammacin Afirka musamman daga Timbuktu.


From Wikipedia, the free encyclopedia · View on Wikipedia

Developed by Nelliwinne