Ahmadu Ali

Ahmadu Ali
Rayuwa
Haihuwa Idah, 1 ga Maris, 1936 (88 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Harsuna Turanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Ahmadu Adah Ali (an haife shi ranar 1 ga watan Maris, 1936) hafsan sojan Najeriya ne mai ritaya, likita kuma ɗan siyasa. An haife shi a garin Idah, Masarautar Igala.[1] Ali ya taɓa zama mataimakin daraktan kula da lafiya na sojoji kuma babban likitan bada shawara na asibitin sojoji dake Kaduna. A shekarar 1973 ya zama Darakta-Janar na farko na Hukumar Kula da Matasa ta Kasa, muƙamin da ya riƙe har zuwa shekarar 1975 lokacin da aka naɗa shi Ministan Ilimi. Ya kuma zama shugaban kwamitin ayyuka na jam’iyyar PDP na ƙasa daga 2005 zuwa 2007.[2][3]

  1. "Ahmadu Ali: Profile in Patriotism". AllAfrica. 12 March 2005. Retrieved 27 December 2015.
  2. Henry Umoru (19 January 2014). "Tukur's many sins and a President's dilemma". Vanguard. Retrieved 27 December 2015. Dr. Ahmadu Ali, from Igala, Kogi State, succeeded Ogbeh.
  3. Jeremy Laurance (24 October 2005). "Nigerian President's wife dies after plastic surgery operation in Spain". The Independent. Archived from the original on 2015-01-30. Retrieved 27 December 2015. "The mother of the nation is gone," wrote Dr. Ahmadu Ali, national chairman of the ruling People's Democratic Party (PDP) in a hastily arranged condolence register at the State House, Abuja.

From Wikipedia, the free encyclopedia · View on Wikipedia

Developed by Nelliwinne