![]() | |
---|---|
![]() | |
Bayanai | |
Gajeren suna | G5S |
Iri |
intergovernmental organization (en) ![]() ![]() |
Ƙaramar kamfani na | |
Mulki | |
Hedkwata | Nouakchott |
Subdivisions | |
![]() | |
Tarihi | |
Ƙirƙira | 16 ga Faburairu, 2014 |
![]() ![]() ![]() |
G5 Sahel ko G5S (French: G5 du Sahel) wani tsari ne na cibiyoyi don daidaita hadin gwiwar yanki a cikin manufofin ci gaba da al'amuran tsaro a yammacin Afirka. An kuma kafa ƙungiyar ne a ranar 16 ga watan Fabrairun shekarar 2014 a Nouakchott, Mauritania,[1] a taron ƙasashe biyar na Sahel: Burkina Faso, Chadi, Mali, Mauritania, da Nijar.[2] An karɓi yarjejeniyar kafa ƙungiyar a ranar 19 ga watan Disamba 2014,[3] kuma ƙungiyar na da mazauni na din-din-din a Mauritania. An shirya haɗin kai akan matakai daban-daban. Babban hafsan hafsoshin ƙasashen duniya ne ke gudanar da aikin soja a ƙungiyar. Manufar G5 Sahel ita ce karfafa dankon zumunci tsakanin ci gaban tattalin arziki da tsaro,[4] tare da yaƙi da barazanar ƙungiyoyin jihadi da ke ta'addanci a yankin ( AQIM, MOJWA, Al-Mourabitoun, da Boko Haram ).
A ranar 15 ga watan Mayun shekarar 2022 ne kasar Mali ta sanar da ficewa daga cikin kawancen, sakamakon kin amincewar da wasu kasashe suka yi na ganin kasar ta karbi ragamar shugabancin kasar [5].