| ||||
Iri |
aukuwa car bombing (en) ![]() | |||
---|---|---|---|---|
Kwanan watan | 20 Mayu 2014 | |||
Wuri | Jos | |||
Ƙasa | Najeriya | |||
Adadin waɗanda suka rasu | 118 | |||
Adadin waɗanda suka samu raunuka | 56 |
A ranar 20 ga watan Mayun shekara ta 2014, wasu bama-bamai biyu sun tashi a birnin Jos na jihar Filato a Najeriya, inda suka kashe mutane aƙalla 118 tare da jikkata wasu fiye da 56.[1] Bam na farko ya tashi ne a wata kasuwa, na biyu kuma kusa da wata tashar mota. Ko da yake babu wata ƙungiya ko wani mutum da ya ɗauki alhakin kai hare-haren, ana danganta hare-haren da ƙungiyar Boko Haram,[2] wacce tayi ƙaurin suna na kai hara hare da dama a Najeriya, musamman yankin arewa maso gabashin ƙasar.
<ref>
tag; no text was provided for refs named BBC