Mutum mutumin wani daga cikin sarakunan Beninhotunan masarautar bennin
Masarautar Benin, wacce kuma ake kira daular Edo, ko kuma daular Benin (Bini: Arriọba ɗo ) wata masarauta ce a yankin kudancin Najeriya a yanzu.[1] Ba ta da dangantaka ta tarihi da jamhuriyar Benin ta zamani,[2] wacce aka fi sani da Dahomey daga karni na 17 har zuwa shekara ta 1975. Masarautar Benin babban birnin jihar ita ce Edo, wacce a yanzu ake kiranta da birnin Benin a jihar Edo, Najeriya. Masarautar Benin ta kasance "ɗaya daga cikin tsofaffin jihohin da suka fi ci gaba a gabar tekun yammacin Afirka". Ta girma ne daga Masarautar Edo da ta gabata ta Igodomigodo a wajajen karni na 11 miladiyya, [3] kuma ta daɗe har zuwa lokacin da Daular Burtaniya ta mamaye ta a shekarar 1897.
↑Bradbury, R. E. (16 August 2018), "Continuities and Discontinuities in Pre-colonial and Colonial Benin Politics (1897–1951)", Benin Studies, Routledge, pp. 76–128, doi:10.4324/9781351031264-4, ISBN 978-1-351-03126-4, S2CID 159119713, retrieved 27 January 2023